Thursday, August 06, 2020

Yobe za ta bude makarantu a ranar Asabar


Gwamnatin jihar Yobe ta sanar cewa za ta bude makarantu a ranar Asabar 8 ga watan Agusta.


Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Ma’aikatar Ilimin Firamare da Sakandaren jihar ta wallafa a shafinta na Facebook a ranar Laraba.

Sanarwar ta bayyana cewa daliban aji 3 na babbar Sakatare da daliban karamar Sakatare na makarantun kwana za su koma a ranar Asabar din 8 ga watan Agusta, yayin da daliban makarantu masu zaman kansu kuma za su koma a ranar Talatar 11 ga watan Agusta 2020.

Ma'aikatar a jawabin ta kuma shawarci daliban da su sanya takunkumin fuska. Tana mai shawartar hukumomin makarantun da su samar da matakan kariya game da annobar Covid-19

Kwamishinan ma'aikatar Dr. Muhammad Sani Idris ya bayyana cewa gwamnatin jihar karkashin jagorancin gwamna Mai Mala Buni ta tabbatar da cewa a ko da yaushe za ta bi umarnin daukan matakan kariya da gwamnatin tarayya ta gindaya.

Har wa yau kwamishinan ya bukaci daliban aji 3 na babbar Sakataren da su kintsa tsaf domin tunkarar jarabawar WAEC da za a fara a ranar 17 ga watan Agusta 2020 domin samun kyakkyawan sakamako ta yadda jihar za ta yi alfahari


No comments:

Post a Comment