
A zamanta na jiya Alhamis, majalisar dokoki ta jihar Yobe, ta dakatar da sabon babban Khadi na jihar Khadi Ibrahim Ahmad daga mukaminsa.
Dakatarwar ta biyo bayan wata takardar korafi da Khadi Shu'aibu Talba ce ya gabatar wa kwamiti mai sa ido akan harkar shari'a na majalisar, inda a cikinta yake kalubalantar cancantar Ahmad.
Khadi Talba har wa yau a korafin nasa ya bayyana wa majalisar cewa kuskure a nada Khadi Ahmad matyayin Babban Khadi, yana mai cewa tun da dai ya girme shi ta fuskar aiki.
Ya kuma kwatant hakan da cewa wata makarkashiya ce ake kokarin kullawa.
Ra'ayoyi dai sun banbanta a zauren majalisar, inda wasu mambobi ke ganin Khadi Ibrahim Ahmad ne ya cancanci mukamin na babban Khadi na jihar ta Yobe, yayin da wasu mambobin ke ganin cancantar hakan akan Khadi Talba.
Tuni dai majalisar ta dakatar da Khadi Ahmad har sai an gudanar da bincike, inda a nan take kakakin majalisar Hon. Usman Adamu ya kafa wani kwamiti da zai gudanar da bincike akan lamarin.
An kuma bukaci kwamitin da ya gabatar da rahoton binciken nasa a ranar 14 ga wannan wata na Yuni lokacin da 'yan majalisar zasu dawo zama. -Dailytrust newspaper of 3 june 2011
No comments:
Post a Comment