Dandalin Shu'aibu Abdullahi Sa'eed Nguru,na yi wa daukacin abokan huldarsa ban gajiya,tare da murnar farawa da kuma kawo karshen babban zaben 2011 lafiya.
Dandalin na Shu'aibu,har wa yau na taya ilahirin 'yan uwa da abokanan arzikinsa,musamman masu sha'awar harkokin siyasa murnar nasarar da jam'iyyunsu suka samu a zabukan da suka gabata,kamar yadda yake taya sauran dangi takaicin rashin nasarar jam'iyyunsu a lokacin zaben,tare da fatan Allah ya ba su dangana,ya kuma sa haka shi ne mafi alheri,amin.
Hakazalika wannan Dandali,na taya dukkanin al'umar kasar nan,musamman wandada suke a yankin arewaci,alhinin abubuwan da suka faru kwanakin baya,dangane da rikicin da ya biyo bayan zaben shugaban kasa,lamarin ya janyo hasarar rayuka,da dukiyoyi masu tarin yawa,wasu kuma dubban jama'a suka rasa matsugunansu! Allah ya kiyaye faruwar haka nan gaba,ya kuma jikan musulman da suka rasa rayukansu,sa'annan ya ba wa iyalansu hakurin jure rashin. Kamar yadda Dandalin ke addu'ar Allah ya ba wa wadanda su ka sami raunuka a sakamakon rikicin lafiya.
Daga karshe,Dandalin na taya shugabannin da aka zaba murna,tare da yi musu addu'ar Allah ya ba su damar sauke nauyin da ya rataya a wuyansu na talakawa. Allah ya taimake mu,ya kuma albarkaci jiharmu ta Yobe,da kasarmu Najeriya baki daya,amin. Na bar ku lafiya.
No comments:
Post a Comment