
A karon farko tun bayan da ta sha kashi a zabubbukan 'yan majalisar tarayya da na wakilain da aka gudanar a Asabar din da ta gabata,babbar jam'iyyar adawa ta PDP a jihar Yobe,ta bayyana cewa ita ce za ta lashe sauran zabukan da suka rage.
Daraktan yakin neman zaben Sen. Usaman Albishir a 2011 na unguwar Bulabulin,a karamar hukumar Nguru,Alh. Muhammadu Kyallomi ne ya bayyana haka,jiya a wani taro da jam'iyyar ta gudanar a makarantar firamare ta Girgiri dake unguwar
ta Bulabulin.
Alh. Kyallomi,ya kuma kara da cewa,ta la'akari da yadda talakawan Yobe suke bukatar canji,da kuma yadda PDPn ta karbu a wajen jama'ar jihar,ko shakka babu PDPn ita za ta yi nasara a zubuka masu zuwa,ya kuma ce amfani da karfin mulki akan masarautun gargajiya da jam'iyyar ANPP mai mulki ta yi,wajen tursasawa jama'ar karkara zabarsu,ta hanyar yi musu barazanar karbe gonakinsu,ko shanunsu,ko gidajensu,idan suka zabi wani,ya ce shi ne musabbabin rashin nasararsu. Alh. Muhammadu Kyallomi,ya kuma gode wa matasa dangane da yadda suka fito kwai da kwarkwata suka zabi PDPn,kazalika ya bukace su da su sake fitowa a zaben ranar Asabar don zabar jam'iyyar ta PDP.
No comments:
Post a Comment