Kwamitin shari'ar addinin Muslunci a Nguru (Nguru Shari'a Implementation Committee) zai tattauna kan al'amuran auratayya wacce ake gani ta tabarbare a tsakanin al'uma.
Wani mamban kwamitin Malam Muhammad Sani Alhasan ya rubuta a shafinsa na Facebook a ranar Asabar cewa, ganarwar za a gudanar da ita ne a yau Lahadi a masallacin Juma'a na kofar fada da misalin karfe 10 na safe, inda za a tattauna batun manyan matsaloli 2 da suka yi wa aure dabaibayi tare da lalubo hanyoyin magance su.
Malam Alhasan ya ce 'yan kwamitin za su tattauna batun matsalolin aure da kuma tsirface-tsirfacen da a cewarsa su suke janyo tsadar aure.
Wasu da dama dai na ra'ayin cewa rashin fahimtar hakikanin aure kafin yin sa, da kwadayi da babban buri, tare kirkirarrun al'adun aure na taka muhimmiyar rawa wajen karuwar mace-macen aure da raguwar yinsa a tsakanin matasa.

No comments:
Post a Comment