Mafi yawancin daliban ajin karshe na makarantun karama da babbar Sakandare a jihar Yobe a yau Talata sun koma makarantunsu, inda a wasu makarantun har aka fara gabatar musu da darussa.
A Larabar da ta gabata ne gwamnatin jihar Yobe ta ba da izinin sake bude makarantun Sakandare domin daliban ajin kashe su dauki jarabawar karshe ta WASSCE.
Wakilin wannan Dandali a yau Talata ya kewaya wasu makarantu a Nguru, ya kuma ba da labarin cewa dalibai da dama sun koma, inda har a wasu makarantu aka gudanar da darussa.
A makarantar gwamnati ta Haya Islam inda wannan Dandali ya fara ziyarta, an martaba ka'idojin matakan kariya da gwamnatin tarayya ta dingaya.
Wani Malamin makarantar da ya bukaci a boye sunansa a zantawarsa da wannan Dandali ya nuna jin daÉ—insa da bude makarantun.
Yana mai korafin cewa tsarin da a ka yi na bitar karatuttukan yaran a cunkushe yake.
A sauran makarantu ma a garin, wasu rahotanni sun nuna cewa lamarin bai sauya ba, yayin da a wasu kuma aka samu tsaiko kafin a gama gwajin zafin jikin dalibai.
A tuna cewa, a Litinin din mako mai zuwa 17 ga watan Agusta 2020 ne daliban makarantun Sakandare a fadin kasa za su fara daukar jarabawar karshe ta WASSEC da hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma WAEC ke shiryawa.



No comments:
Post a Comment