Tuesday, August 11, 2020

Malaman Sakandare a Yobe sun shiga aji a karan farko bayan sake bude makarantu

Mafi yawancin daliban ajin karshe na makarantun karama da babbar Sakandare a jihar Yobe a yau Talata sun koma makarantunsu, inda a wasu makarantun har aka fara gabatar musu da darussa.

A Larabar da ta gabata ne gwamnatin jihar Yobe ta ba da izinin sake bude makarantun Sakandare domin daliban ajin kashe su dauki jarabawar karshe ta WASSCE.

Wakilin wannan Dandali a yau Talata ya kewaya wasu makarantu a Nguru, ya kuma ba da labarin cewa dalibai da dama sun koma, inda har a wasu makarantu aka gudanar da darussa.

A makarantar gwamnati ta Haya Islam inda wannan Dandali ya fara ziyarta, an martaba ka'idojin matakan kariya  da gwamnatin tarayya ta dingaya.

Wani Malamin makarantar da ya bukaci a boye sunansa a zantawarsa da wannan Dandali ya nuna jin daÉ—insa da bude makarantun.

Yana mai korafin cewa tsarin da a ka yi na bitar karatuttukan yaran a cunkushe yake.

A sauran makarantu ma a garin, wasu rahotanni sun nuna cewa lamarin bai sauya ba, yayin da a wasu kuma aka samu tsaiko kafin a gama gwajin zafin jikin dalibai.

A tuna cewa, a Litinin din mako mai zuwa 17 ga watan Agusta 2020 ne daliban makarantun Sakandare a fadin kasa za su fara daukar jarabawar karshe ta WASSEC da hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma WAEC ke shiryawa.

No comments:

Post a Comment