Tuesday, July 09, 2019

An kaddamar da neman takarar Hon. Sani Garba Sharu ta shugancin karamar hukumar Nguru a PDP a ranar Litinin


Daruruwan 'yan jam'iyyar PDP ne maza da mata a ranar Litinin suka taru a babban dakin taro na kamfanin Lasanco dake Nguru domin halartar babban taron kaddamar da neman takarar Hon. Sani Sharu ta shugancin karamar hukumar Nguru a karkashin jam'iyyar.

Wakilin wannan Dandali ya sami halartar babban taron ya kuma ba da labarin cewa 'yan jam'iyyar PDP sun goyi bayan mai neman takarar.

An kuma gabatar da jawabai daban-daban a wurin taron yayin da da dama daga mahalarta taron suka tashi cikin murna.

A jawabinsa ga 'yan jam'iyyar a wurin taron, mai neman takarar shugancin karamar hukumar Nguru Hon. Sani Sharu ya bayyana kudurorinsa da ya ce idan aka zabe shi zai samar wa mutanen Nguru.

Hon. Sani kamar yadda wani na hannun damarsa Habu Salisu ya jaddadawa wannan Dandali, ya yi alkawarin cewa zai samar da ci gaban da suka hada da:

1. Kirkiro wani tsari da zai taimaka wajen inganta ilimin karamar hukumar.

2. Sannan ya samar wa matasan karamar hukumar hanyoyi na musanman wajen dogaro da kai.

3. Zai yi duk mai yiwuwa wajen hada kan matasa ta hanyar wasu daburu na musanman domin ci gaban Nguru.

4. Zai inganta fannin lafiya da suka kunshi haihuwa kyauta a daukacin karamar hukumar.

5. Akwai kuma shiri na musanman na raya karkara domin jin dadin 'yan karamar hukumar.

Hon. Sani a jawabin ya kuma godewa mahalarta taron da daukacin 'yan karamar hukumar Nguru, yana mai addu'ar samun nasara a zaben kananan hukumomi mai zuwa.

No comments:

Post a Comment