Tuesday, August 21, 2018

Wajibin iyaye ne da su isar da amanar 'ya'yan da Allah ya ba su— Hudubar Idin babbar Sallah

An yi kira ga iyaye da su zama masu kishin iyalansu wajen kula da tarbiyyarsu domin samun tsira da samun al'uma tagari da kuma tsira a gidan duniya da na lahira.

A wani sako da kwamitin shari'a a Nguru ya aika wanda Limamin masallacin Idi na Kwalejin Atiku Abubakar da ke Nguru Al- Sheikh Umar Jinjiri da a ka fi sani da Iya da baba ya karanta yayin hudubarsa ta Sallar Idin babbar Sallah yau a garin Nguru.

Malamin ya ce wajibi ne ga iyaye da su tsare amanar da Allah ya ba su ta 'ya'ya domin samun tsira gidan duniya da lahira.

A sakon kazalika Al- sheikh Iya da baba ya bayyana cewa koke-koken da ke ta karuwa a tsanin al'umomi na bacin tarbiyya sun hada da yawaitar zinace-zinace da shaye-shaye da kuma neman maza.

Malamin ya ci gaba da cewa ba dalili ba ne al'umomi su zuba idanu ana aikata fasadi domin wai ana takamar 'yanci.

Yana mai tsawatar wa iyayen game da fadin manzon Allah na  wajibcin kawar da fasadi akan al'umomi domin gudun halaka ta gaba daya.

No comments:

Post a Comment