Wednesday, September 13, 2017

GWAMNATIN SAUDIYYA TA YANKEWA WANI MAHAJJACI DAN JIHAR SOKOTO WATANNIN UKU A GIDAN YARI


Wata kotun shari’ar Musulunci da ke zaman ta a kasar Saudiyya ta yanke wa wani mahajjaci Mallam Mamman Kwa-Kwazo hukuncin zaman Gidan kaso har na tsawon watanni uku.

Malam Mamman wanda dan asalin karamar hukumar Goronyo ne da ke jihar Sokoto, gwamnatin kasar ta same shi da lafin yin karya da mallakar wata jakar kudi da aka tsinta wadda kuma ba tashi ba ce.

Da yake tabbatar da faruwar al’amarin sakataren karamar hukumar Goronyo Lawal 'Yar-Tsakuwa, cewa ya yi, mahajjacin ya tsinci jakar kudin ne a harabar masallacin a ranar juma’a da ta gabata.

Rahotannin sun ce Mallam Mamman Kwa-kwazo tun da fari yaki amincewa ya bayar da jakar kudin ga mamallakinta, wanda hakan ne ya sanya aka garzaya da shi ga jami’an tsaro.

A cewar Sakataren ba a san inda bakon Gidan yarin ya fito ba, sai daga baya ne aka mika shi sansanin mahajjatan jihar Sokoton, bayan an tabbatar da cewa daga karamar hukumar da ta fito daga yankin yake, yanzu haka dai gwamnatin kasar Saudiyya ta dakatar da Mamman Kwa-kwazo shiga kasar har na tsawon watanni biyar.

No comments:

Post a Comment