Thursday, June 22, 2017

TSAKANINMU DA GWAMNA SAI GODIYA — In ji wasu ma'aikatan Yobe


Mai girma Gwamnan jihar Yobe Alh. Ibrahim Gaidam

Wasu ma'aikata a jihar Yobe na ci gaba da nuna godiyarsu ga gwamnatin jihar sakamakon albashinsu da ta biya su tun daga yanzun domin yin hidimar Sallah.

A tattaunawarsu da wannan Dandali jim kadan bayan sun sami albashinsu a garin Nguru, ma'aikatan suka ce hakan ya kara musu karfin gwuiwar da su ma za su yi bushasha sosai a bukukuwan Sallar bana.

Tun a jiya Laraba ne dai ma'aikatan suka fara ganin sakon biyansu hakkokinsu, inda saura suka karbi nasu sakon a yau Alhamis.

Wani ma'aikaci a Nguru da ya ce a boye sunansa ya ce, hakan abin a yaba ne kuma yana godewa Gwamna Ibrahim Gaidam.

Ya kara da cewa, abinka da dan albashi kullum yana cikin taraddadin ko ta wacce hanya ce zai warware matsaloli, musamman ma a irin wadannan lokuta da ake batar da kudade wajen yin hidimomi.

Ya ce, amma da zuwan wannan albashi to ka gani ai hakan zai taimaka matuka.

Kazalika wani ma'aikacin da shi ma ya ce a boye sunansa ya bayyana godiyarsa ce ga gwamna Ibrahim Geidam.

Yana mai yin kira ga gwamnan da ya duba batun yiwuwar biyan kudaden hutun nan da ake ta yayata labarinsu a 'yan lokutan baya.

Har wa yau ya kuma yi kira ga gwamnatocin kananan hukumomi da su yi koyi da gwamnatin jihar wajen biyan ma'aikatansu hakkokinsu kafin ranar Sallah.

Da ma dai tun da farko, gwamnatin jihar ta fada ta bakin kakakinta Alh Abdullahi Begu a wani bayani da Abubakar Ibn Usman ya nakalto a shafinsa na facebook a safiyar Laraba 21/06/017, cewa tini mai aikatar kudi ta jihar har ta aika da kudaden maikatan zuwa bankuna domin bayarwa

No comments:

Post a Comment