Wednesday, September 14, 2016

ASUU ZA TA TSINDIMA YAJIN AIKIN GARGADI A RAN 2 GA OKTOBA MAI ZUWA



Kungiyar malaman jami`o`i ta kasa ASUU, ta yi barazanar shiga yajin aikin gargadi daga ranar 2 ga watan Oktoba mai zuwa.

A cikin wani jawabi da kungiyar ta fitar a Litinin din nan mai dauke da sa hannun shugaban kungiyar na reshen jami`ar Abuja Mr. Ben Ugheoke, kungiyar ta ce gwamnatin tarayya ta gaza wajen sake komawa teburi tattaunawa da shgabannin kungiyar domin ganin an aiwatar da alkawuran da gwamnatin ta dauka a 2009 na inganta jami`o`in kasar.

Jaridar Premium Times ta nakalto jawabin yana cewa, ``mun yi kokarin ganin cewa gwamnati ta saurare mu, to amma sai muka fahimci cewa gwamnatin na wasa ne kawai da hankulanmu,  a saboda haka ne muka kudiri aniyar shiga yajin aikin gargadi na tsawo mako guda, daga ranar  2 ga watan Oktoban nan mai zuwa, domin  nunawa gwamnati cewan mu ba da wasa muke ba``.

Jawabin ya ci gaba da cewa, ``za mu shiga yajin aiki na sai baba ta gani, idan har gwamnati ta kasa yin wani abu na azo a gani bayan mun kamala yajin aikin gargadi ``.

Idan dai  za a iya tinawa,  a shekara ta 2009 ne gwamnatin tarayyar Najeriya, ta dauka wa uawar kungiyar ta ASSU wasu alkawuran inganta jami`o`in kasar, wanda kawo yanzu a cewa ASSUn, kasha 30 bisa 100 ne na alkawuran kawai gwamnatin ta aiwatar.



No comments:

Post a Comment