![]() | |
| Daga hagu, Hon. Shu'aibu Danladi Hamza, sai Alh. Auwalu Dogo |
Bayanai na cewa, dan majalisa mai wakiltar
Nguru ta tsakiya Hon. Shu`aibu Danladi Hamza, ya raba gari da wasu kusoshin
jam`iyyarsa ta APC, wadanda ake bayyana su a matsayin silar ci zabensa a
shekara ta 2011 da 2015.
Shugaban matasan jam`iyyar APC na karamar hukumar Nguru, Alh.
Auwalu Dankwanyo, wanda aka fi sani da Auwal Dogo, tare da shugaban jam`iyyar na yankin Hausari Alh. Auwalu Kiliya na daga
cikin wadanda `yan sanda suka tsare domin amsa tambayoyi.
Shugabannin biyu dai na zargin Hon.
Shu`aibu Danladi Hamza ne da hannu akan tsare su da `yan sandan suka yi a ranar
Talatar da ta gabata a Gashu`a.
Ba a san dai ko menene dalilan dan
majalisar na raba gari da wadannan jiga-jigai ba. Domin kokarin jin ta
bakinsa da wannan Dandali ya yi ya cutura.
To sai dai kuma wannan Dandali, ya sami zantawa
da daya daga cikin wadanda aka tsare Alh. Auwalu Dogo, wanda ke zargin dan majisar da hannu a kange su da `yan sandan suka
yi har na sama da awoyi 7 ba tare da an saurare su ba.
Ga dai bayanin da Alh. Awal Dogo ya yi wa wannan Dandali:
`` … Gaskiya ne sha'aibu danladi hamza
yayi duk abinda zaiyi wajen ganin anyi mana walakanci na karshe, ranar talata
13/09/2016 Mai martaba sarkin nguru ya gaiyace mu cin abinci no Auwalu dogo
youths leader Nguru tare party chairman APC na Hausari auwalu kiliya, munzo
kofar fada latti ana fitowa sai ga sha'aibu danladi tare da ari maidami
chairman nguru sai auwalu kiliya yace hon yaya za ayi ahmadu mirwa yabawa duka
party chairman na nguru out side 30k amma mu hudu na cikin gari ka hana mu laifin
me mukayi maka kuma kabawa wasu wanda ma sun yakeka lokacin zabe, ana cikin
haka sai aka fara ruwa sai nace kyaleshi kazo mu tafi ai zamu hadu, shikenan
sai washe gari akaxo da hilux da yan sanda da bindiga aka kamamu akaje aka rufe
mu a cell har tsawon awa bakwai sai Sen Ahmed Lawan yayi sannan aka fito damu
misalin karfe 11.00 pm akace muje gobe mudawo. Tunda muka shiga hannun hukumar
yan sanda baizo ba sai waya kawai yakeyi babu ruwansa damu da yanda ne. Wannan
shine abinda yafaru ``.
Daga nan sai Auwal Dogo ya ci gaba da cewa `` ...Kuma yau (Asabar) munje area command na police gashua tun misalin 8.00am muna jira sai da karfe 2.00 pm akace wai muyi under taking babu mu babu shi, police suka rubuta undertaking akan babu ruwan mu dashi. wannan shine abinda yafaru ayau 17/09/2016. ``.
Wasu da wannan Dandali ya zanta da su a garin Nguru, na dora alhakin
rabuwar kan dan majalisa Shu`aibu Danladi Hamza. Mutnen suka ce wananan butulci
da abin kunya ne, duba da yadda a cewarsu, mutanen suka yi ruwa da tsaki domin
ganin dan majilisar ya ci zabe a lokaci da ake yakin neman zabe, yayin da wasu
ke ganin an yi gajen hakuri, da an kai zuciya nesa, a cewarsu da ba ta kai ga an
yi hakan ba.

No comments:
Post a Comment