Monday, September 12, 2016

AN BUKACI MUSULMAI A KWANAKIN SALLAH DA SU DAGE DA ADDU`O`IN SAMUN SASSAUCIN KUNCIN RAYUWA



Kwamitin shari`a a Nguru jihar Yobe, ya yi kira ga al`umar Musulmai, da su himmatu cikin wadannan ranakun Sallah masu girma wajen yin addu`o`in neman sassauci daga Allah SWT, game da kuncin rayuwar da ake ciki.

A sako da ya rarraba zuwa ga masallatan Idi a Nguru, kwamitin ya kuma ja hankulan matasa dasu guji aikata munanan dabi`u da ka iya jefa su da al`uma cikin matsaloli a lokacin shagulgulan Sallah.

Da yake karanta sakon kwamitin a Litinin din nan bayan an idar da Sallah, limamin Masallacin Idi na Kwalejin Atiku Abubakar dake Nguru, Al-Sheikh Umar Jinjiri ya ce, tilas ne matasa su yi la`akari da halin da ake ciki wajen domin su kiyaye kansu daga aikata barna da ka iya janyo ta jefa al`uma cikin hadari
.
Da ma dai tun da farko, a daren jajiberen jiya Lahadi, mahukunta a garin Nguru suka bad a snarwar dakatar da zirga-zirgar abubuwan hawa, tun daga karfe 6:00 na safe har zuwa 4:00 na yamma.

No comments:

Post a Comment