Kwamitin shari`a a Nguru jihar Yobe, ya yi kira ga al`umar Musulmai, da su himmatu
cikin wadannan ranakun Sallah masu girma wajen yin addu`o`in neman sassauci daga Allah SWT, game da kuncin rayuwar da ake
ciki.
A sako da ya rarraba zuwa ga masallatan Idi a Nguru, kwamitin ya kuma ja
hankulan matasa dasu guji aikata munanan dabi`u da ka iya jefa su da al`uma cikin
matsaloli a lokacin shagulgulan Sallah.
Da yake karanta sakon kwamitin a Litinin din nan bayan an idar da Sallah,
limamin Masallacin Idi na Kwalejin Atiku Abubakar dake Nguru, Al-Sheikh Umar
Jinjiri ya ce, tilas ne matasa su yi la`akari da halin da ake ciki wajen domin su kiyaye
kansu daga aikata barna da ka iya janyo ta jefa al`uma cikin hadari
.
Da ma dai tun da farko, a daren jajiberen jiya Lahadi, mahukunta a garin
Nguru suka bad a snarwar dakatar da zirga-zirgar abubuwan hawa, tun daga karfe
6:00 na safe har zuwa 4:00 na yamma.

No comments:
Post a Comment