
Jam'iyyar ANPP mai jan ragamar mulkin jihar Yobe,ta ce daga dukkanin alamu,ANPP ita zata sake danewa karagar mulkin jihar,a babban zabe mai zuwa.
Shugaban jam'iyyar ANPP na jihar,Alh. Sani Inuwa Nguru ne ya bayyana haka,lokacin zantawarsa jiya da wakilin jaridar Leadership,a gidansa dake garin Damaturu.
Inuwa wanda kuma ya kara da cewa "idan aka lura da yanayin siyasar yanzu,to fa babu shakka suke da Nasara".
Kazalika ya yi nuni akan irin tazarar da jam'iyyar tasa ta yi wa P.D.P a jihar. A cewarsa "muke da gwamna,da mataimakin gwamna,tare da 'yan majalisar jihar 19 daga 24,kuma kowannensu ba ya shakkar mutanensa".
Ya kuma ce "ai tun farkon kafuwar Dimukradiyyar nan, a shekarar 1999,P.D.P ba ta taba yin Nasara ba,ba kuma ta yi Nasarar ba,mu kadai za mu yi ta mulki a jihar har abada.- Leadership Newspaper.
No comments:
Post a Comment